in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu dakaru sun yi garkuwa da yara da dama a Sudan ta Kudu
2015-02-22 16:33:18 cri
A jiya Asabar 21 ga wata, asusun taimakon yara kanana na MDD wato UNICEF ya ba da sanarwar cewa, wasu dakaru da ba a san su wane ne ba sun yi garkuwa da yara 89 a Malakale, babban birnin dake kasar Sudan ta Kudu.

UNICEF din ya yi bayanin cewa, da farko wadannan dakaru sun taru a wani matsuguni, daga baya suka ruga a guje cikin gidajen matsugunin inda suka tara yaran tare da yin garkuwa da yaran da yawancin su ba su wuce shekaru 12 da haihuwa ba.

Wakilin asusun na UNICEF a Sudan ta Kudu, Jonathan Fitch ya bayyana cewa, wannan danyen aiki ya keta dokokin kasa da kasa. Yin garkuwa da yara da sa su shiga rikicin dakaru, hakan zai lalata iyalai da zaman al'umma baki daya.

An fara rikici a kasar Sudan ta kudu tun daga watan Disamba na shekarar 2013, wadanda suka haddasa mutuwar mutane sama da dubu 10, yayin da wasu sama da miliyan daya suka rasa gidajensu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China