in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta bukaci Amurka da ta mutunta batutuwan da suka shafi dokokinta
2015-03-05 20:12:04 cri
Kwanan baya, majalisar gudanarwa ta kasar Amurka ta nuna cewa, ya kamata kasar Sin ta saurari ra'ayin kasarta a yayin da Sin ta kafa daftarin dokar yaki da ta'addanci. Dangane da lamarin, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana a yau cewa, kafa dokar yaki da ta'addanci harkar cikin gidan kasar Sin ce, babu bukatar ta saurari ra'ayoyin kasashen ketare, haka kuma, kasashen ketare ba su da ikon matsa lamba ga kasar Sin kan wannan harkar, don haka kasar Sin na fatan kasar Amurka za ta mutunta batutuwan da suka shafi yadda kasar Sin ke kafa dokokinta.

Bugu da kari Hua Chunying ta jaddada cewa, matakan da kasar Sin ta dauka domin kiyaye tsaron bayanai sun dace da ka'idar dokokin gudanar da mulki, sun kuma dace da akidar gamayyar kasa da kasa, bugu da kari, matakan ba za su kalubalanci moriyar 'yan kasuwa da ke mu'amula da intanet ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China