in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Akwai bukatar daukar matakan bai daya wajen yaki da ta'addanci, in ji manzon kasar Sin
2014-12-20 16:12:04 cri
Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Liu Jieyi, ya ce akwai bukatar kasashen duniya su dauki matakan bai daya, tare da kaucewa nuna banbanci, ko wariya a yakin da ake ci gaba da yi da ta'addanci.

Mr. Liu wanda ya bayyana hakan a jiya Jumma'a ya kuma kara da cewa, alakanta ta'addanci da wata kabila, ko wani addini, ba zai haifar da kyakkyawan sakamakon da ake fata ba.

Ya ce a wasu yankunan Afirka, ayyukan ta'addanci na da nasaba da kungiyoyi masu aikata manyan laifuka na kasa da kasa, don haka ya dace a fuskanci yaki da ta'addanci da manufofin da suka dace.

Game da hadin gwiwa a wannan fage kuwa, Mr. Liu ya ce ya zama wajibi gamayyar kasashen duniya su tallafawa kasashen Afirka, a fannin horas da jami'an tsaro, da tsaron iyakoki, da kuma yaki da masu safarar miyagun kwayoyi.

Har wa yau ya ce akwai bukatar maida hankali ga dakile laifukan dake shafar kasa da kasa ta hanyar amfani da fasahar sadarwa.

Wakilin na kasar Sin ya ce a matsayin Sin na kasar da ke yaki da nata nau'in ta'addanci, tana da burin ganin kasashen Afirka sun samu zarafin fuskantar wannan matsala ta irin nasu yanayi, za kuma ta ci gaba da hada kai da su, da ma sauran kasashen duniya, a yunkurin dakile ayyukan ta'addanci, da sauran laifukan da suka shafi kasa da kasa. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China