in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira ga kasashen duniya da su kara hadin gwiwa wajen yaki da ta'addanci
2015-02-19 16:23:02 cri
Shugaban kwamitin sulhun MDD na wannan wata, kuma zaunannen wakilin Sin a MDDr Liu Jieyi, ya ce ya zama wajibi kasashen duniya su kara hada kai waje guda, su kuma bi tsari daya, tare da aiwatar da hadin gwiwa da kasar Libya, da ma sauran yankuna da kasashe, wajen yaki da ta'addanci.

A jiya Laraba ne dai Liu Jieyi ya kira wani taron kwamitin sulhun MDD, inda aka nazarci yanayin da ake ciki a kasar Libya. Kaza lika kwamitin sulhun ya saurari rahoton da wakilin musamman na babban sakataren MDD kan batun Libya Bernardino Leon ya gabatar ta kafar bidiyo.

Taron dai ya samu halartar ministocin harkokin wajen Libya, da Masar, da wakilin kasar Algeria, inda suka gabatar da jawabai. Har wa yau mambobin kwamitin sulhun sun yi wata ganawar sirri game da halin da kasar Libiya ke ciki.

Jim kada da kammala taron, Liu ya bayyana cewa, membobin kwamitin sulhun sun yi Allah wadai da danyen aikin da kungiyar 'yan ta'adda ta IS ta yi, na kashe wasu Misirawa wadanda ta yi garkuwa da su, tare da mika sakon ta'aziya ga gwamnatin Masar da iyalan wadanda aka hallaka.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China