in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Iraki ya sanar da daukar manyan matakan soja kan arewacin kasar
2015-03-02 15:35:01 cri

Wani jami'in tsaro na kasar Iraki ya bayyana cewa, sojojin kasar sun kai farmaki ga birnin Dour na jihar Salahudin dake arewacin kasar a jiya Lahadi, kuma suna shirya murkushe dakarun kungiyar IS da suka yi kaka gida a wannan jiha.

Wannan jami'i ya kara da cewa, sojojin Iraki sun yi amfani da tankunan yaki da manyan boma-bomai da rokoki masu cin gajeran zango, a yayin da suke kai farmaki kan birnin Dour dake da nisan kilomita 150 daga birnin Bagadaza da kuma yankunan dake dab da shi, abin da ya yi sanadiyyar lalata gine-gine da dama. Sabo da jerin farmaki da kuma gargadin daukar matakan soja ya sa galibin mazaunan wurin suka tsere daga gidajensu. A halin yanzu kuma, babu kowa a cikin wannan birni. A sa'i daya kuma, wani reshen sojojin Iraki yana kan hanyar zuwa birnin Tuz-Khurmato na jihar Salahudin, domin yanke hanyar jigilar kayayyaki na dakarun dake wurin, tare da yi musu kawanya.

A wannan rana, shugaban hukumar tsaron jihar Salahudin Sheikh Jasim al-Jbarra ya ce, firaministan kasar Iraki Haider al-Abad ya sanar a daren wannan rana a birnin Samarra dake arewacin kasar cewa, an fara daukar manyan matakan soja a hukunce kan dakarun kungiyar IS a jihar Salahudin.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China