in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Iraqi ya yi kira da a dunkule domin tunkarar ta'addanci
2014-12-29 11:01:04 cri

Firaministan kasar Iraq Haider al-Abadi ya roki kasashe dake yankin Gabas ta Tsakiya da su yi aiki kafada da kafada domin karfafa fafutukar da suke yi na yaki da matsalar ta'addanci.

Abadi, ya yi wannan kalamin ne a cikin wata sanarwa bayan ya gana da mataimakin firaministan kasar Kuwaiti Sheikh Sabah Al-khaled Al-Hamad Al-Sabah, wanda ya kawo ziyara aiki a kasar ta Iraqi.

Abadi ya kara da cewar, kara bunkasa tattalin arziki, tare da habbaka dankon zumunta a tsakanin kasashen dake yankin, wani abu ne da zai iya karawa jama'a karfin gwiwa tare da nesanta jama'a daga barazanar ta'addanci da tsatsauran ra'ayi.

A nashi jawabin, mataimakin firaministan Kuwaiti ya ce, kasar Iraq muhimmiyar kasa a yankin, kuma sauran kasashe a shirye suke su hada kai domin tunkarar kalubalen dake gaba. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China