in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jaridar People's Daily ta Sin ta ci gaba da inganta tunanin fannoni hudu da shugaban kasar ya fidda
2015-03-01 16:54:31 cri
Yau Lahadi 1 ga watan Maris, jaridar People's Daily ta ba da wani sharhi mai taken "gudanar da harkokin jam'iyyar kwaminis ta Sin yadda ya kamata ta yadda za a iya gina shuwagabannin kasar masu karfi", ya zuwa ranar, jaridar ta riga ta kashe kwanaki biyar wajen bayyana da kuma inganta tunanin nan na fannoni hudu da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gatabar da suka hada da gina zaman takewar al'umma mai cike da arziki daga dukkan fannoni, zurfafa gyare-gyare a gida daga dukkan fannoni, gudanar da harkokin kasar bisa dokoki da kuma gudanar da ayyukan jami'yyar kwaminis ta Sin yadda ya kamata.

Cikin sharhin da People's Daily ta fitar a yau Lahadi, an ce, cikin tunanin fannoni hudu da shugaba Xi Jinping ya sanar, gudanar da ayyukan jami'yyar kwaminis ta Sin yadda ya kamata na nuna aniyar hada harkokin jam'iyyar da harkokin kasa tare, ya kamata a gudanar da harkokin jam'iyyar bisa babban tsarinmu yadda ya kamata, yayin da ake ci gaba da nuna manufofin jam'iyyar bisa fannoni daban daban, lamarin ya biya bukatun jam'iyyar kwaminis ta Sin da jama'ar kasar baki daya.

Kaza lika, sharhin ya nuna cewa, jagoranci na jam'iyyar kawaminis shi ne tushen tunanin fannoni hudu, babban alhakin 'yan jam'iyyar kwaminis shi ne na tsayawa tsayin daka wajen gudanar da harkokin jam'iyyar yadda ya kamata da kuma daga dukkan fannoni, ta yadda jam'iyyar za ta iya kasancewa babban karfi na ba da jagoranci, tare da tabbatar da cimma burinmu na farfadowar kasa ta Sin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China