in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya jaddada batun kwaskwarima da gudanar da harkokin kasa bisa doka
2014-11-03 16:05:32 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jaddada muhimmancin gudanar da aikin kwaskwarima da gudanar da harkokin kasa bisa doka. Shugaba Xi ya bayyana hakan ne yayin wata ziyara da ya kai lardin Fujian a kwanakin baya.

Xi ya ce kamata ya yi a yi biyayya ga kudurorin cikakken zama na uku da na hudu, na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, da sa kaimi ga samun wadata a kasar, da yin kwaskwarima a dukkan fannoni, da kuma gudanar da harkokin kasa bisa dokoki, da kiyaye bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewar al'ummar kasar, da kuma kara samun ci gaba.

Xi Jinping ya nuna cewa, kara kyautata halayen 'yan jam'iyyar kwaminis ta Sin, da daukar tsauraran matakai wajen gudanar da harkokin jam'iyyar yadda ya kamata, kana su ne tushen gudanar da ayyuka a dukkan fannoni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China