in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sa kaimi ga batun gudanar da harkokin kasa bisa doka na da ma'ana sosai ga samun makoma mai kyau a kasar Sin, in ji wasu mutanen ketare
2014-10-26 17:29:10 cri
A gun cikakken zama na hudu na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta Sin karo na 18 da aka rufe a ranar 23 ga wata, an zartas da 'kudurin kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin kan manyan batutuwa dangane da sa kaimi wajen gudanar da harkokin kasa bisa doka daga dukkan fannoni'. Wasu manyan jami'an ketare suna ganin cewa, sa kaimi ga batun gudanar da harkokin kasa bisa doka daga dukkan fannoni na da ma'ana sosai wajen samun makoma mai kyau a nan kasar Sin, kuma Sin za ta ci gaba da samun bunkasuwa a sabili da hakan.

Dan majalisar dokokin kasar Birtaniya, Charles Powell ya bayyana cewa, sa kaimi ga batun gudanar da harkokin kasa bisa doka, wani babban ci gaba ne da Sin ta samu a fannin kafa dokoki. A yayin da Sin ke zurfafa gyare-gyare, dole ne Sin ta kara inganta rawar da dokoki ke takawa. Ya ce, wannan babban masomi ne na Sin wajen kyautata dokokin kasar.

Babban manazarci dake aiki a hukumar Brookings ta Amurka, Kenneth Liberthal ya bayyana cewa, wannan cikakken zaman taro ya kasance taro na farko da JKS ta dauki 'gudanar da harkokin kasa bisa doka' a matsayin babban taken taron. Rahoton taron ya bayyana hanyar da Sin za ta bi wajen samun ci gaba, da kokarin kasar na kyautata dokoki da kara sa haske a ciki, domin kaucewa sa hannu da wasu kungiyoyi da jami'ai za su yi. Wannan cikakken zaman taro ya samar da sabon karfi da sabuwar hanya wajen cimma wannan buri cikin yakini.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China