in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
JKS ta lashi takwabin hukunta wadanda ke kokarin kawo baraka a cikin jam'iyya
2014-12-29 20:11:29 cri
Kwamitin tsakiya na hukumar kula da harkokin siyasa ya jaddada bukatar da ke akwai ta daukar matakan ladabtarwa kan wadanda ke kokarin kawo baraka a cikin jam'iyya da nufin cimma muradunsa maimakon na jam'iyya.

An bayyana hakan ne cikin wata sanarwar da JKS ta bayar a karshen wata ganawa da kwamitin tsakiya na hukumar kula da harkokin siyasa ya gudanar a yau, inda aka nuna irin matakan da ake dauka wajen magance batun cin hanci da rashawa.

Bugu da kari sanarwar ta ce, kamata ya yi a kara daukar matakai game da matsayin da jam'iyya ke dauka kan manyan jami'ai da mambobin jam'iyya na bin dokoki kamar yadda aka tsara.

Taron wanda shugaba Xi Jinping ya jagoranta ya kuma tsayar da ranar 12 zuwa 14 ga watan Janairu a matsayin ranakun da za a gudanar da taro na 5 na hukumar ladabtawar da jam'iyya karo na 18. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China