in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ba za ta amince da cinikin hauren giwa ba
2015-02-26 20:14:24 cri
Kwanan baya, kungiyar kare dabbobi ta kasar Burtaniya ta mika sako ga shugabannin kasar Sin, inda ta yi kira ga shugabannin kasar da su taimaka wajen hana cinikin hauren giwa a kasar ta Sin, a kokarin da ake na rage yawan giwayen da ake kashewa a nahiyar Afirka.

Dangane da lamarin, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya bayyana a yau Alhamis cewa, kasar Sin ba ta yarda da cinikin hauren giwa ba bisa doka ba ko kadan, kuma kasar za ta ci gaba da hada kai da gamayyar kasa da kasa don ganin an hana kashe giwaye da kuma cinikin haurensu ba bisa doka ba, kana ta yi kira ga kasashen duniya da su hada kai wajen ganin an kare giwaye. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China