in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren harkokin waje na Amurka ya yi gargadi da ci gaba da saka takunkumi ga kasar Rasha
2015-02-22 17:05:00 cri
Sakataren harkokin waje na Amurka, John Kerry ya ce kasarsa da aminanta wasu kasashen Turai suna la'akari da kara kakaba takunkumi ga kasar Rasha, yayin da shugaban Amurka Barack Obama yake la'akari da karin matakan da zai dauka kan batun Ukraine.

Bayan ganawarsa da ministan harkokin waje na Birtaniya Philip Hammond, a ranar Asabar din nan a birnin Landan, John Kerry ya bayyana cewa, a cikin 'yan kwanaki masu zuwa, shugaba Obama zai yi la'akari da matakan da za a dauka, daga bisani, a san me za'a yi a nan gaba. Wadannan matakai sun hada da ko za a bayar da makamai ga sojojin Ukraine ko a'a, da kuma kara sanya takunkumi ga Rasha sabo da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da tayi.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China