in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Barack Obama ya yi maraba da cimma matsaya tsakanin Amurka da Rasha kan daidaita batun makamai masu guba na Syria
2013-09-15 16:39:28 cri
A ranar Asabar 14 ga wata, shugaban kasar Amurka Barack Obama ya yi maraba da rattaba hannu kan yarjejeniyar daidaita batun makamai masu guba na Syria tsakanin Amurka da Rasha, tare da bayyana cewa, idan ba za a cimma burin lalata wadannan makamai masu guba na Syria ta hanyar diplomasiyya ba , to, Amurka za ta dauki matakai.

Shugaba Obama ya nuna cewa, wannan yarjejeniya za ta taka muhimmiyar rawa wajen sanya wadannan makamai a karkashin kulawar kasashen duniya, ta yadda har ma za a lalata su a karshe. Mista Obama ya kara da cewa, Amurka za ta ci gaba da yin hadin gwiwa tsakaninta da Rasha, Birtaniya, Faransa, MDD da kuma sauran bangarorin da abin ya shafa, a kokarin warware wannan batu yadda ya kamata.

A sa'i daya, shugaba Obama ya ce, idan gwamnatin Syria ta ki bin yarjejeniyar, ya kamata a hukunta ta. Idan kuma hanyar diplomasiyya ba za ta daidaita wannan matsala ba, Amurka za ta dauki matakai.

A ran 14 ga wata, sakataren harkokin waje na Amurka John Kerry da takwaransa na Rasha Sergei Lavrov sun daddale wata yarjejeniya dangane da hallaka makamai masu guba na Syria a Geneva bayan sun shafe kwanaki uku suna tattaunawa. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China