in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afirka ta Kudu na tsara dokar hana 'yan kasashen ketare mallakar filaye kasar
2015-02-15 10:27:26 cri
A jiya ne fadar shugaban kasar Afirka ta Kudu ta bayar da wata sanarwa, inda ta bayyana cewa, kasar Afirka ta Kudu tana tsara wata dokar hana 'yan kasashen ketare mallakar filaye a kasar, amma an amince a ba su hayar filayen har na tsawon shekaru 30 zuwa 50. Sanarwar ta bayyana cewa, wannan doka ta kayyade cewa, yawan filayen da jama'ar kasar za su mallaka ba zai zarce hekta dubu 12 ba, idan ya zarce haka, gwamnati za ta kwace su ta sake raba su. Kana dokar ta haramtawa 'yan kasashen waje hayar filayen dake shafar kiyaye muhalli ko tabbatar da tsaro ko na tarihi da al'adu ko wadanda ke da nasaba da manyan tsare-tsaren kasar.

A nan gaba ne ake sa ran mika dokar ga majalisar ministocin kasar Afirka ta Kudun don yin muhawara a kan ta, kana daga baya a ji ra'ayoyin jama'ar kasar kan wannan doka, daga bisani kuma a mika ta ga majalisar dokokin kasar don ta zartas da ita, kana a karshe shugaban kasar zai sanya mata hannu.

Sanarwar ta bayyana cewa, kayyade filayen da 'yan kasashen ketare za su mallaka wani batu ne da aka amince da shi a fadin duniya, kuma an tsara doka game da wannan lamari ne don tabbatar da tsaron yankunan kasa da batun samar da abinci a kasar Afirka ta Kudu, kana za a warware matsalar rashin daidaito kan rarraba filayen kasar bayan da aka kawar da tsarin mulkin mallaka da nuna wariyar launin fata da aka aiwatar a kasar na fiye da tsawon shekaru 300. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China