in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Jordan ta kashe Sajida al-Rishawi ta kungiyar IS
2015-02-04 16:19:39 cri
A yau da safe ne ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Jordan ta bayar da sanarwa cewa, Jordan ta riga ta kashe Sajida al-Rishawi da kungiyar IS ta bukaci a yi musayar ta da matukin jirgin saman nan dan kasar ta Jordan, kana ta kashe wani dan kungiyar al-Qaeda.

A jiya ne, bangaren sojan kasar Jordan ya tabbatar da cewa, kungiyar IS ta kashe matukin jirgin sama dan kasar mai suna al- Kasasbeh da ta yi garkuwa da shi, bangaren soja na kasar Jordan ya ce, zai mayar da martani mai karfi ga wannan lamari.

Bayan da aka samu labarin kisan al- Kasasbeh, sarki Abdullah na II na kasar Jordan dake ziyara a kasar Amurka ya dakatar da ziyarar tasa bayan da ya yi shawarwari tare da shugaban kasar Amurka Barack Obama inda ya koma gida.

Ana zargin Sajida al-Rishawi da hannu a hare-haren kunar bakin wake da aka kai cibiyar ciniki ta kasar Jordan dake birnin Amman, inda fiye da mutane 60 suka mutu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China