in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen BRICS sun zartas da jadawalin hadin gwiwar kan batun yawan al'umma
2015-02-14 17:07:30 cri
Jiya Jumma'a 13 ga wata, an rufe taron ministocin kasashen BRICS kan batun yawan al'umma, watau taron manyan jami'ai da masana kan batun yawan al'umma zagaye na biyu a kasar Brazil, inda aka zartas da jadawalin hadin gwiwar batun yawan al'umma na kasashen BRICS.

An fara taron a ran 11 ga wata, inda ministoci da masana da suka zo daga kasashen Sin, Brazil, India, Rasha da kuma Afirka ta Kudu suka tattauna kan batutuwan da suka shafi mata da yara, yin rigakafi kan cututuka masu yaduwa da cutar kanjamau, kaurar mutane daga karkara zuwa birane, tsufan al'umma, nuna bambanci ga maza da mata cikin kasuwannin neman aikin yi da dai sauransu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China