in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi shawarwari tsakanin ministocin harkokin waje na kasashen BRICS
2014-09-26 16:48:53 cri
Ministan harkokin waje na kasar Sin Wang Yi ya halarci shawarwari tsakanin ministocin harkokin waje na kasashen BRICS a ranar Alhamis 25 ga wata yayin babban taron MDD.

A yayin shawarwarin, Mr. Wang ya nuna cewa, ganawar tsakanin shugabannin kasashen BRICS da aka yi a bana a Fortaleza ta samar da sabon zarafi ga tsarin kungiyar. Don haka ya kamata bangarorin daban-daban mahalartan taron su yi amfani da wannan zarafi domin tsai da shirin hadin kan tattalin arziki nan gaba tsakaninsu.

Ministocin mahalartan taron sun kai da matsaya daya cewa, a wannan yanayin da ake ciki, ya kamata kasashen BRICS su kara hadin gwiwa tsakaninsu, ta yadda za su zurfafa dangantakar sada zumunci ta fuskar tattalin arziki da ciyar da hadin kai ta fuskar ciniki, tattalin arziki da zuba jari gaba. Ban da haka kuma, ya ce kamata ya yi a kara hadin kai ta fuskokin yaki da ta'addanci a duniya, magance cutar Ebola, matsalolin da suka shafi Palasdinu, da Ukraine da sauransu, da kuma kiyaye zaman lafiya da tsaron duniya tare. Kazalika, ya kamata a goyi bayan MDD da ta shirya bukukuwan tunawa da cikon shekaru 70 da aka kafa kungiyar, da kuma samu nasarar kawo karshen yakin duniya na biyu, da dukufa kan kiyaye zaman oda na duniya mai adaci da daidaici karkashin tsarin mulkin MDD. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China