in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin ya kira taron zaunannen kwamitin majalisar gudanarwa
2015-01-28 20:59:56 cri
A yau ne firaministan kasar Sin Li Keqiang ya jagoranci taron zaunannen kwamitin majalisar gudanarwa, kan gaggauta aikin fitar da kayayyakin kasar zuwa ketare, da suka hada da layin dogo, tashar nukiliya ta samar da wutar lantarki da dai sauransu, ta yadda za a iya ciyar da hadin gwiwar makamashi na kasa da kasa gaba, tare da kuma raya ayyukan hadin gwiwar kasa da kasa.

A yayin wannan taro, an ce, ya kamata a fitar da kayayyakin kasar Sin zuwa kasashen ketare kamar yadda ake bukatarsu wajen gina kayayyakin kasashen da kuma neman bunkasuwa, sa'an nan gwamnatin ta ciyar da wannan aikin gaba, a yayin da wasu kamfanoni ke gudanar da aikin. Kana, fitar da manyan kayayyaki da kuma fasahohin zamani na kasar Sin zuwa ketare ya dace da moriyar juna, ba ma kawai zai iya habaka damar hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya ta kasa da kasa ba, haka kuma zai iya kyautata ayyukan masana'antun kasar Sin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China