in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin Huawei ya yi bikin gwajin na'urorin sa ido na bidiyo a kasar Kamaru
2014-08-12 11:06:12 cri
Kamfanin Huawei da kamfanin sadarwa na kasar Kamaru, sun yi hadin gwiwar gudanar gwajin na'urorin sa ido na bidiyo a dukkanin fadin kasar Kamaru, bikin da ya gudana a cibiyar bada umurni ta hukumar wakilan tsaron kasar dake birnin Yaounde.

Bisa labarin da jaridar Tribune ta kasar Kamarun ta fitar, ta ce gwajin wanda ya gudana a kwanakin baya, ya bada damar nazartar amfani da fasahar sadarwa ta 4G, domin inganta karfin na'urorin na sa ido a kasar ta Kamaru. Za kuma a kafa na'urorin sa idon kimanin 70 a sassan birane shida da suka hada da Yaounde, da Douala, da Waza da dai sauransu. Kana an ce cikin na'urorin akwai wadanda ka iya daukar bidiyo daga nisan kilomita 5. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China