A cewar wannan jami'i mayakan an kasha su lokacin wani hari da aka kai masu a maboyar su dake Amchide a arewacin kasar dake kan iyaka da Najeriya da misalin karfe 8 na daren alhamis agogon wajen.
Majiyar ya ce kusan mayakan su 400 suka kai hari ma sojojin kamaru da jami'an tsaron kasar a lokacin wannan arangama an kasha mayakan kusan 180 sai dai ba bu wanda ya rasa ransa a bangaren sojojin kasar.(Fatimah Jibril)