in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 74 sun mutu a kasar Kamaru a sakamakon cutar kwalara
2014-08-11 14:30:26 cri
Tun daga barkewar cutar kwalara a arewacin kasar Kamaru a watan Afrilu da ya gabata, mutane 74 sun mutu a sakamakon haka sannan wadansu fiye da 1600 sun harbu da shi.

Gidan telebijin na Kamaru ya ruwaito ministan kiwon lafiya kasar Mama Fouda Andre na cewa, tun daga barkewar annobar ta kwalara, an samu yawanci masu fama da ita a yankin arewacin kasar, musamman a jihar Far North. Ya zuwa ranar Talata ta makon jiya 6 ga watan nan, an gano mutane 1609 da suka kamu da annobar ta kwalara a jihar Far North, a ciki kuma 74 sun rasa rayukansu. A halin yanzu, an gano mutane biyu masu fama da cutar a jihar Littoral dake kudu maso yammacin kasar.

Ana ta samun barkewar cutar ta kwalara a kasar Kamaru a wadannan shekaru, musamman a shekarar 2010 da ta 2011. A lokacin, aka samu barkewar cutar mai tsanani a jihohi da dama, wanda ya sa gwamnatin kasar ta nemi taimako daga hukumar kiwon lafiya ta duniya wato WHO da sauran hukumomin duniya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China