in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministocin Rasha, Jamus, Ukraine da kuma Faransa sun yi tattauna ta wayar tarho kan rikicin Ukraine
2015-01-03 17:09:23 cri
Ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergei Lavrov ya zanta da takwarorinsa na kasar Jamus Frank Walter Steinmeier, da na Ukraine Pavlo Klimkin, da kuma na kasar Faransa Laurent Fabius ta wayar tarho, game da matakan da ya dace a dauka domin ciyar da yunkurin da ake yi, na warware rikicin gabashin kasar Ukraine gaba.

Rahotanni daga ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Rasha na cewa, ministoci hudu sun jaddada bukatar gaggauta sake kiran taron wanzar da ci gaba, na tawagar kasar Ukraine, da kungiyar tsaro da hadin gwiwar kasashen Turai, da kuma kasar Rasha.

Kaza lika ministocin hudu sun tattauna kan ci gaban shawarwarin da kasashen suke gudanarwa da bangarori daban daban da wannan batu ya shafa.

Ya zuwa yanzu dai bangarori daban daban da batun kasar ta Ukraine ya shafa, sun amince da a ci gaba da ba da taimako wajen warware rikicin kasar ta Ukraine a siyasance.

Bisa kididdigar da hukumar MDD mai lura da wannan batu ta fitar, alkaluma sun nuna cewa, daga tsakiyar watan Afrilun bara ya zuwa yanzu, rikicin gabashin kasar ta Ukraine ya hallaka akalla mutane 4707, yayin da wasu sama da 10,000 suka jikkata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China