in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masanan hukumar WHO sun yaba da ayyukan cibiyar sa ido kan mutanen da suka kamu da cutar Ebola ta kasar Sin dake kasar Saliyo
2014-12-26 10:51:36 cri
A kwanakin baya, masanan hukumar kiwon lafiya ta duniya wato WHO sun kai ziyara cibiyar da ke sa ido kan mutanen da suka kamu da cutar Ebola ta kasar Sin dake kasar Saliyo, inda suka tattauna da likitocin dake cibiyar.

A ganin masanan, akwai isassun na'urori a cibiyar, kuma ana gudanar da ayyuka bisa ka'idojin hukumar WHO, don haka suka yaba da ayyukan da cibiyar ta gudanar.

Ya zuwa ranar 24 ga watan Disamba, cibiyar ta karbi mutane 544 da aka zaton sun kamu da cutar Ebola, yayin da mutane 230 daga cikinsu aka tabbatar sun kamu da cutar, kuma aka kawar da mutane 217 daga cikinsu da ake zaton sun kamu da cutar .(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China