in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar ta bayyana kudurinta na bunkasa hadin gwiwar dake tsakaninta da Sin
2014-12-19 20:24:55 cri
A jiya ne shugaban kasar Masar Abdel Fattah el-Sisi ya bayyana cewa, kasar Masar tana son ci gaba da inganta hadin gwiwar dake tsakanin kasarsa da kasar Sin, da kuma ciyar da dangantakar hadin gwiwa dake tsakanin kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare gaba, haka kuma kasar Masar tana son yin koyi da fasahohin kasar Sin na neman bunkasuwa.

Bisa gayyatar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi masa, shugaba Abdel Fattah el-Sisi zai kawo ziyarar aiki kasar Sin ranar 22 zuwa 25 ga wata, kuma wannan ita ce ziyarar aiki ta farko da shugaba el-Sisi zai kawo kasar Sin tun bayan da ya hau karagar mulkin kasar.

Abdel Fattah el-Sisi ya ce, zai yi amfani da wannan ziyara wajen karfafa dangantakar dake tsakanin kasarsa da kasar Sin, tare da janyo karin hankulan kamfanonin kasar Sin da su zuba jari a kasar.

Bugu da kari, ya jaddada cewa, ya kamata a raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu bisa ka'idojin neman bunkasuwa da kuma kiyaye zaman lafiya, ta yadda zai dace da moriyar jama'ar kasashen biyu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China