in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya jaddada matsayinsa kan yaki da ta'addanci
2014-10-25 16:59:06 cri
Jiya Jumma'a 24 ga wata da dare, kwamitin sulhu na MDD ya fidda wata sanarwa, inda ya yi allah wadai da harin ta'addanci da aka kai a lardin Sinai na arewa dake kasar Masar a wannan rana, tare da jaddada cewa, zai ci gaba da tsayawa tsayin daka wajen yaki da ta'addanci bisa ka'idojin kundin tsarin MDD.

A ran 24 ga wata, an kai harin boma-boman da aka dana cikin motoci a wata tashar binciken soja dake lardin Sinai na arewa na kasar Masar, wanda ya zuwa yanzu, ya haddasa rasuwar sojojin kasar a kalla 30, yayin da wasu suka jikkata.

Dangane da lamarin, shugaban kasar Masar Abdelfattah al Sisi ya sa hannu kan wani kuduri a wannan rana da dare, inda ya sanar da cewa, tun ranar 25 ga wata, wasu wuraren dake arewacin lardin Sinai za su shiga yanayin ko ta kwana na watanni uku, a lokacin, za a kafa dokar hana fitar dare a wuraren tun karfe biyar na dare zuwa karfe bakwai na safe a ko wace rana.

Bugu da kari, ta bakin kakakinsa, babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya ba da wata sanarwa a ran 24 ga wata da dare, inda ya yi alla wadai da harin ta'addanci da aka kai a lardin a wannan rana. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China