in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kotu a Masar ta soke hukuncin da aka zartaswa Hosni Mubarak
2014-11-30 16:41:31 cri
Wata babbar kotun daukaka kara a Masar, ta soke hukuncin daurin rai da rai, da aka zartas kan tsohon shugaban kasar Hosni Mubarak, wanda a baya aka yankewa hukunci bisa zargin kisan daruruwan masu zanga-zanga, yayin boren da ya kai ga kifar da gwamnatinsa a shekarar 2011.

Kotun ta kuma kori shari'ar da ake yi wa wasu manyan jami'an tsohuwar gwamnatin tasa, ciki hadda tsohon ministan cikin gida na gwamnatin Habeb Al-Adly, da karin wasu jami'an su 6 da aka zarga da ba da umarnin kisan masu boren.

Baya ga batun kisan masu zanga-zangar, kotun ta kuma wanke Mubarak da ministan mai a gwamnatinsa daga zargin aikata cin hanci, mai alaka da iskar gas da Masar din ta fitar zuwa Isra'ila a wancan lokaci.

A shekarar 2012 ne dai wata kotun hukunta manyan laifuffuka a kasar ta yanke wa Mubarak hukuncin na daurin rai da rai, kafin daga bisani ya daukaka kara.

Shugaba Mubarak wanda a yanzu haka ke zaman jarun na shekaru 3, sakamako wani laifi na cin hanci da rashawa, shi ne shugaban kasar Masar na farko da aka zartaswa hukunci a shari'ar da aka shafe shekaru 4 ana gudanarwa. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China