in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rikici ya barke a tsakanin kungiyoyin tsagerun Libya
2014-12-14 16:54:43 cri
Jiya Asabar 13 ga wata, an yi rikici mai tsanani tsakanin kungiyoyin tsageru biyu a wani wurin dake kusa da tashar jiragen ruwa ta Sidra dake kasar Libya, domin neman iko kan tashar jiragen ruwa dake fitar da man fetur ta Sidra mafi girma a kasar, inda kuma har yanzu ake ci gaba da rikicin tsakanin bangarorin biyu.

Tattalin arzikin kasar Libya dai na dogaro da man fetur inda kasar take samun kudaden shiga na sama da kashi 95 bisa 100 na man fetur din da take fitowar zuwa kasashen ketare.

Tun ranar 13 ga watan Yuli, ake ci gaba da samun ricike-rikice tsakanin kungiyoyin biyu a babban birnin Tripoli da birnin Banghazi da wasu biranen kasar, haka kuma sakamakon rikice-rikicen, gwamnatin wucin gadi da sabuwar majalisar dokokin kasa dake wakiltar jama'ar kasar sun kaura zuwa karamin birnin Tobruk dake gabashin kasar. Bugu da kari, kungiyar tsagerun dake goyon bayan addini, ta taimaka wa majalisar dokokin kasar da aka riga kawo karshen wa'adinta farfado da mulkinta, bayan da kungiyar ta mamaye birnin Tripoli, ta kuma kafa wata sabuwar gwamantin tsaron kasa. Lamarin da ya sa, a halin yanzu, akwai gwamnatoci biyu da kuma majalisun dokokin biyu dake kasancewa a kasar Libya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China