in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 450 sun rasa rayukansu sakamakon tashe-tashen hankula a kasar Libya
2014-12-01 15:40:07 cri
Jami'in hukumar kiwon lafiya a kasar Libya, sun bayyana cewa dauki ba dadi na kusan wata guda tsakanin dakarun kungiyoyi biyu a birnin Banghazi, ya haifar da kisan mutane a kalla 450.

Rahotanni sun bayyana cewa daga ranar 15 ga watan Oktoba ya zuwa wannan lokaci, dakarun kungiyoyin 'yan ba ruwanmu masu goyon bayan gwamnatin wucin gadi ta kasar Libya, sun yi gumurzu da nufin kwace ikon mallakar birnin Banghazi, sun kuma fafata da dakarun fararen hula na kungiyar masu kishin addini.

Wani jami'in asibiti a birnin na Banghazi ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu mutane a kalla 450 ne suka rasu sakamakon wadannan rikice-rikicen, ciki har da mayaka da kuma fararen hula.

Jami'in ya kara da cewa, ana samun alkaluman yawan gawawwakin wadanda suka rasa rayukansu daga asibitoci da dama a birnin na Banghazi. Sai dai ya ce da yake dakarun kungiyar masu kishin addini ba sa kai mambobinsu da suka rasu, ko suka samu raunuka zuwa asibiti, yawan mutanen da suka mutu a sakamakon rikice-rikicen, a hakika ya zarce mutum 450. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China