in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 142 sun mutu biyowa bayan tashe-tashen hankula a garin Kikla dake kasar Libya
2014-11-04 10:58:01 cri
Wani jami'in hukumar kula da lafiya ta kasar Libya ya bayyana cewa, wasu sassan dakarun fararen hula 2 sun yi musayar wuta a 'yan kwanakin nan, a garin Kikla dake yamma da birnin Tripoli, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane a kalla 142.

Ya ce a ranar 10 ga watan Oktoba, dakarun Zintan dake goyon bayan kungiyar 'yan ba ruwan mu sun kai hari ga garin Kikla, mai nisan kilomita kimanin 150 da birnin Tripoli, wanda kuma ke karkashin ikon dakarun Fajr Libya dake goyon bayan kungiyar masu kishin addini.

Wani mutum dake aiki a wani asibitin dake garin Kikla ya ce rikicin na ranar 3 ga wata, ya haddasa mutuwar mutane a kalla 142, baya ga wasu kimanin 518 da suka jikkata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China