A cewar wata sanarwa da kakakinsa ya gabatarwa 'yan jarida, sakatare janar zai gana a cikin wannan rana da mataimakin shugaban majalisar dokokin Libiya da kuma mambobin zauran wakilai da suka janye daga zaman tarurukan majalisar dokoki.
Ministan harkokin wajen kasar Italiya, har ma da wakilan musammun na sauran kasashe za su halartar wannan taro.
Ziyarar shuagaban MDD, ta zo daidai bayan nasarar kokarin wakilinsa na musammun, da kuma tawagar MDD dake kasar Libiya (MANUL) domin sake maido da tattaunawa tsakanin 'yan majalisun kasar. Wannan tattaunawa da aka fara a ranar 29 ga watan Satumba, an kafa ta bisa tushen ka'idojin gaskiya, kaucewa nuna bambanci da watsi da ta'addanci, kuma ta kasance shirin farko wajen warware rikicin kasar. (Maman Ada)