An dai gudanar da taron ne a hedkwatar ma'aikatar lafiyar kasar dake birnin Abuja. Kana taron ya samu halartar jakadan Sin dake kasar Gu Xiaojie, da mai bada shawara game da harkokin ciniki na ofishin jakadancin Sin Zhou Shanqing, da karamin ministan lafiya na Nijeriya Khaliru Alhassan, da kuma sauran jami'ai da dama.