in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin zai halarci taron koli na G20 a Australiya
2014-11-07 16:42:35 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping zai halarci taron koli na kungiyar G20 karo na tara da zai gudana a watan Nuwamban bana a birnin Brisbane na kasar Australiya, kana zai kai wani rangadin aiki a kasashen Australiya, New Zealand da kuma Fiji. Taron zai gudana a ranakun 15 da 16 ga wata, kana rangadin aikin shi kuma zai gudana a ranakun 16 da 23 ga wata, in ji kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Qin Gang a ranar Jumma'a.

Shugaba Xi Jinping zai gana da shugabannin kasashen yankin Pasifik dake da huldar diplomasiyya tare da kasar Sin, in ji mista Qin

Mista Xi zai yi wannan rangadi bisa goron gayyatar babban gwamna da faraministan kasar Australiya Peter Cosgrove da Tony Abbott, da kuma babban gwamna da faraministan New Zealand Jerry Mateparae da John Key, da kuma shugaba da faraminstan kasar Fiji Epeli Nailatikau da Voreqe Bainimarama. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China