in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a sa kaimi ga kafa yankin tattalin arziki na hanyar siliki, in ji shugaban Sin
2014-11-06 20:36:56 cri
A safiyar Talata 4 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kira taro karo na 8 na rukunin ba da jagoranci kan tattalin arziki da cinikayya na kwamitin tsakiyar JKS, inda aka yi nazari kan yin fasali ga yankin tattalin arziki na hanyar siliki da hanyar siliki a yankin teku na karnin 21, da kafa bankin zuba jari kan manyan kayayyakin amfanin jama'a na Asiya da asusun raya hanyar siliki.

A yayin taron, shugaba Xi ya yi jawabinsa mai muhimmanci, inda ya jaddada cewa, kafa yankin tattalin arziki na hanyar siliki da hanyar siliki a yankin teku na karnin 21 ya dace da bukatar zamani da burin kasa da kasa na neman samun bunkasuwa, kuma ya bayar da wani babban dandalin bunkasuwa mai kunshe da sassa daban daban, wanda yake da dogon tarihi da babban tushen al'adun bil'adam, a sabili da haka, ya iya hada da tattalin arzikin Sin dake bunkasa cikin sauri da moriyar sauran kasashen dake dab da wannan hanya a gu daya. Kamata ya yi a gudanar da wannan aiki yadda ya kamata, a kokarin sada zumunci da samun amincewa da goyon baya daga kasashen dab da hanyar.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China