in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sanarwar yaki da cin hanci kasashen Sin da Amurka ne suka ba da shawara, inji wani jami'in APEC
2014-11-06 20:45:56 cri

Za'a saka sanarwar yaki da cin hanci a takardun bayan taron kungiyar yin hadin gwiwa a yankin Asiya da tekun Pacific ta fuskar tattalin arziki wato APEC da za a gudana a nan birning Beijing, in ji wani jami'in kungiyar APEC.

Alan Bollard, direktan zartaswa na sakatariyar kungiyar APEC ya ce, sanarwar Beijing da za a bayar game da cin hanci ba shugabannin kasar Sin kadai suka ba da shawarar bayarwa ba, har ma da Amurka.

Mr. Bollard ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai, inda ya kara da cewa, sanarwar za ta haifar da kafa wata kungiya wadda za ta samo hukumomin da za su sa ido a yankin APEC, za ta kuma ba su damar isar da sako a kan ko wane abu ya taso ga saura.

Ya ce, wannan yana da muhimmanci wajen bin diddigin abubuwan dake faruwa a yankin a kuma bi bahasi har a kwato kaddarori idan har an kai su wani wuri ba bisa doka ba.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China