in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zhang Gaoli ya halarci bikin bude taron ministocin kudi na kungiyar APEC karo na 21
2014-10-22 16:13:11 cri

An gudanar da taron ministocin kudi na kungiyar APEC karo na 21 a yau Laraba 22 ga wata a nan birnin Beijing, inda mamban hukumar harkokin siyasa ta kwamitin tsakiya na Jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin kuma mataimakin firaministan kasar Zhang Gaoli ya halarci bikin bude taron.

A cikin jawabin da ya bayar, Zhang Gaoli ya bayyana cewa, wannan taron ministocin kudi wani muhimmin taro ne na kungiyar APEC da ake da shirin gudanarwa a kasar Sin a bana, inda za a tattauna kan halin tattalin arziki da duniya da yankin Asiya da tekun Pasific ke ciki, da yadda za a hada gwiwa kan zuba jari ga ayyukan more rayuwa, da manufofin kudi dake shafar kyautata tsarin tattalin arziki, kana da yadda za a mara baya ga bunkasuwar tattalin arzikin shiyya-shiyya ta hanyar hada-hadar kudi da dai sauransu, wadanda ke da babbar ma'ana a zamanin yau.

Ban da wannan kuma, Zhang Gaoli ya ce, kasar Sin kasa ce a yankin Asiya da tekun Pasific, ba a iya rabawa bunkasuwarta da ci gaban yankin. Kasar Sin za ta yi kwaskwarima da kirkire-kirkire don sa kaimi ga bunkasuwata a fannonin kimiyya da fasaha, tsare-tsare, ayyukan gudanarwa, da kuma salon cinikayyya, a kokarin karfafa zukatan kamfanoni da jama'a wajen raya ayyukansu, ta yadda za a iya samun dauwamammen ci gaban tattalin arzikinta, har ma a kasance a kan gaba. Haka zalika kuma, kasar Sin za ta kara bude kofa ga kasashen waje, da kyautata yanayin cinikayya, domin jawo kamfanonin kasashen waje da su zuba jari a kasar Sin. Bunkasuwar kasar Sin, a cewar Mr. Zhang, za ta kara samar da damar ci gaba ga yankin Asiya da tekun Pasific har ma duk duniya baki daya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China