in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya nada wata tawagar musamman don gudanar da bincike kan aikin kiyaye zaman lafiya
2014-11-01 17:41:08 cri
Babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya nada wata tawagar musamman don gudanar da bincike kan aikin kiyaye zaman lafiyar MDD, a wani mataki irinsa na biyu, da za a gudanar da bincike daga dukkan fannoni kan ayyukan kiyaye zaman lafiyar da MDD ta aiwatar, bayan gudanar makamancinsa karon farko a shekarar 2000.

Yayin taron da aka saba yi, kakakin babban magatakardan MDD Stephane Dujarric ya gabatar da wata sanarwar, inda ya nuna cewa, ya zuwa yanzu, shekaru 15 ke nan, tun bayan gudanar da bincike kan aikin kiyaye zaman lafiyar a karo na farko, don haka aikin kiyaye zaman lafiyar a yanzu na fuskantar karin matsaloli. Baya ga fama da hare-haren da sojojin kiyaye zaman lafiya ke fuskanta.

Hakan a cewar sa ne ya haifar da bukatar gudanar da bincike kan matakan da MDD za ta dauka wajen inganta aikin kiyaye zaman lafiyar da kuma ba da taimako ga kasashen da hare-haren ke shafa yadda ya kamata, da kuma tabbatar da karfin sojojin kiyaye zaman lafiya da na tawagogin siyasa cikin yanayin kasa da kasa mai canzawa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China