in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a jiyar Xinjiang inji mujallar Truth Seeking
2014-07-16 14:25:31 cri
Wani bayani da mujallar "Truth Seeking" ta kasar Sin ta fitar a baya bayan nan ya nuna matukar bukatar da ake da ita, ta tabbatar da wanzuwar yanayin zaman lafiya da lumana a jihar Xinjiang dake Arewa maso yammacin kasar Sin.

Sharhin da wannan mujalla ta buga ya nuna cewa, kasar Sin tana kunshe da kabilu 56, wadanda kuma ke bada gudummawa ga kyakkyawar nasara da ci gaban kasar.

Kaza lika ya bayyana yanayin musamman na gurguzu da kasar Sin ke bi, a matsayin tushen samun ci gaban jama'ar kasar Sin, da kuma moriya ta bai daya ga daukacin kabilun kasar. Kana wannan ce hanyar da kasar ke bi wajen samun wadata, da ci gaba, da kuma kyautatuwar rayuwar jama'a.

Don haka ne mujallar ta bayyana daukar matakan jajircewa, wajen bunkasa kasar Sin bisa halayen musamman na gurguzu, ta yadda za a kai ga samun wadata da ci gaba a kasar, tare kuma da samun kyakkyawar makoma ga jihar Xinjiang. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China