in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar na fatan hada gwiwa da Amurka a fannin yaki da ta'addanci
2014-09-14 17:11:43 cri
Sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry da takwaransa na Masar Sameh Shoukry, sun bayyana cewa kasashen su za su karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu a fannin yaki da ta'addanci.

Jami'an sun bayyana hakan ne dai a jiya Asabar a birnin Alkahira na kasar Masar ya yin wani taron manema labaru na hadin gwiwa da suka gudanar.

Da yake karin haske game da hakan, mista Shoukry ya ce Masar na goyon bayan Amurka a fagen yaki da kungiyar ISIS, da ma sauran kungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi, ta na kuma kira ga sauran kasashen duniya da su goyi bayan wannan kuduri domin cimma nasarar yaki da masu tsattsauran ra'ayi.

A wani ci gaban kuma Mr. Kerry ya gana da shugaban Masar Abdelfattah al Sisi, da babban sakataren kungiyar tarayyar kasashen Larabawa Nabil el-Araby, inda a zantawarsa da shuwagabannin biyu, shugabannin sun nuna cewa, kamata ya yi a kara zage damtse wajen karfafa yakin da ake yi da kungiyoyin 'yan ta'adda.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China