in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta samu nasarori da dama kan aikin kula da magunguna
2014-10-16 14:35:27 cri
A jiya Laraba ne aka gudanar da taron shekara-shekara na kasashe membobin kungiyar shirin hadin gwiwa na sa ido kan magunguna ta hukumar kiwon lafiya ta duniya wato WHO karo na 37 a birnin Tianjin dake kasar Sin, inda wani jami'in rukunin kula da tsaron magunguna na hukumar WHO ya bayyana cewa, kasar Sin ta samu nasarori da dama a aikin sa ido kan ga matsalolin da a kan gamu da su a sakamakon shan magani tare da bada gudummawa ga hadin gwiwar da kasashen duniya ke yi a wannan fanni.

Jami'in ya bayyana cewa, kasar Sin ta gabatar da rahotanni da dama ga tsarin sa ido kan magunguna na duniya. A matsayinta na kasar da ke kan gaba wajen samarwa da cinikin magungunan gargajiya a tsakanin kasa da kasa, kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen sa ido ga matsalolin da a kan gamu da su a sakamakon shan maganin gargajiya.

Mataimakin shugaban hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasar Sin Wu Zhen ya bayyana a gun taron cewa, kasar Sin ta kafa tsarin sa ido na kasa, da na larduna, da kuma na birane.

Game da matsalolin da ake fuskanta, Wu Zhen ya bayyana cewa, kasar Sin ta fara gudanar da aikin sa ido kan magunguna ne bayan sauran kasashen duniya, kuma tana fuskantar kalubale da dama a fannonin kimanta tsaro da hadarin magunguna. Kana yana fatan kasashen duniya za su kara yin hadin gwiwa da mu'amala a wannan fanni don tabbatar da tsaron magunguna tsakanin al'ummominsu tare da kiyaye lafiyar al'ummar duniya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China