in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya zuwa yanzu Sin ta tura likitoci dubu 23 zuwa kasashe da yankuna 66
2013-10-30 16:32:44 cri
Shugaban sashen kula da harkokin kasashen waje na hukumar kula da kiwon lafiya da kayyade yawan al'umma ta kasar Sin Ren Minghui ya bayyana a yau Laraba 30 ga wata a nan birnin Beijing cewa, ya zuwa yanzu, Sin ta tura likitoci dubu 23 zuwa kasashe da yankuna 66.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, ban da tura rukunonin likitoci zuwa kasashen waje, kasar Sin ta bayar da gudummawar na'urorin kiyon lafiya da magunguna, gina asibitoci da sauran cibiyoyin kiwon lafiya, horar da kwararrun kiwon lafiya, da kuma samar da kudi da fasahohi ga kasashe masu tasowa musamman kasashen Afirka. Kana Ren Minghui ya nuna cewa, a cikin 'yan shekarun nan, an fadada hadin gwiwar dake tsakaninsu zuwa fannonin yaki da zazzabin cizon sauro, kula da lafiyar mata da yara da dai sauransu.

Ren Ming Hui ya kara da cewa, kasar Sin za ta ci gaba da nuna goyon baya ga kungiyoyi, asusu da kuma kamfanoni da su shiga a dama da su, da kara yin hadin gwiwa a tsakaninta da sauran abokan hulda da kungiyoyin kasa da kasa, da kuma daukar sabbin matakai wajen sa kaimi ga yin hadin gwiwa a bangaren kiwon lafiya a tsakaninta da kasashen Afirka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China