in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane fiye da dubu 3 sun mutu a sakamakon cutar Ebola, a cewar WHO
2014-09-28 10:28:03 cri
Bisa sabuwar sanarwar da hukumar kiwon lafiya ta duniya wato WHO ta bayar, an ce, mutane fiye da dubu 3 sun mutu a sakamakon cutar Ebola da aka samu a kasashen yammacin Afirka.

A cikin sanarwar, WHO ta yi kashedi cewa, yanzu cutar Ebola tana ci gaba da yaduwa, kuma an samu sabbin mutane 6 da aka tabbatar sun kamu da cutar Ebola a yankin kan iyakar kasa na kasar Liberia dake dab da kasar Cote d'Ivoire. Kana ana gano bullar cutar a sabon yankin kasar Guinea.

Tawagar aiki ta musamman ta kungiyar AU mai kula da harkokin tinkarar cutar Ebola ta tashi zuwa kasar Liberia a ranar 18 ga wata, kuma sauran tawagogi biyu sun shirya tashi zuwa kasar Saliyo da ta Guinea a ranar 5 ga watan Oktoba da kuma karshen watan Oktoba.

Ban da wannan kuma, a ranar 26 ga wata majalisar gudanarwar asusun ba da lamuni na duniya ta amince da samar da kudaden gudummawa dalar Amurka miliyan 130 ga kasashe 3 na yammacin Afirka mafi fama da cutar Ebola. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China