in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zambia tana son ci gaba da raya dangantakar sada zumunci tare da Sin a fannoni daban daban
2014-09-11 15:57:29 cri
Kwanan baya, ministan harkokin wajen kasar Zambia Harry Calabar ya bayyana cewa, dangantakar sada zumunci dake tsakanin kasar Zambia da kasar Sin na ci gaba da kansancewa cikin kyakyyawan yanayi tun lokacin da aka kulla huldar difomasiyya a tsakanin bangarorin biyu a watan Oktoba na shekarar 1964, ya zuwa yanzu, rabin karni ya riga ya wuce, kuma kowane shugaban kasar Zambia na yaba wa kasar Sin cewa, ita ce babbar aminiya ta kasar, haka kuma, a wannan lokacin da muke ciki, kasar Zambia na son ci gaba da habaka dangantakar sada zumunci tsakanin kasashen biyu.

Ya kara da cewa, kasar Sin ta samar da babban taimako ga kasar Zambia a lokacin da take gina layin dogo daga Tanzania zuwa kasar ta Zambia, haka kuma, kasar Zambia ta tsaya tsayin daka wajen taimaka wa kasar Sin kan farfado da babban matsayinta a zauren MDD.

Ya ce, cikin shekaru 50 masu zuwa, kasar Zambia za ta ci gaba da zurfafa hadin gwiwar tsakanin kasashen biyu, kuma Zambia na nuna godiya matuka ga kasar Sin kan yadda take samar wa kasashen Afirka goyon baya bisa bukatunsu ba tare da gindaya wani sharadi ba. Bugu da kari, kasar Sin na da fasahohin zamani masu kyau, kana kasashen Afirka na da albarkatun kasa, shi ya sa, hadin gwiwar bangarorin biyu yake samun ci gaba tare da kuma cimma moriyar juna. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China