in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Zambia ya nuna yabo ga taron dandalin tattaunawa na Boao na Asiya da ake yi a lokacin da ya dace
2013-04-08 15:48:35 cri
Ran 7 ga wata, shugaban kasar Zambia Michael Sata ya ba da jawabi, yayin bikin bude taron shekara-shekara na dandalin tattaunawar Boao na Asiya a shekarar 2013, inda ya nuna yabo ga wannan taron taron da ake gudanar a lokacin da ya dace.

Har ila yau, bisa labarin da aka samu daga jaridar mel ta rana-rana ta kasar Zambia, an ce, yayin taron shekara-shekara na dandalin tattaunawar Boao na Asiya, shugaba Michael Sata ya bayyana cewa, babban jigon taron, wato "neman samun bunkasuwar nahiyar Asiya baki daya, ta hanyoyin yin kirkire-kirkire, da sauke nauyi da kuma yin hadin gwiwa", ya nuna fatan kasashen Asiya sosai, wajen neman bunkasuwa cikin lokutan da suka gabata, da halin da ake ciki, dama nan gaba.

Cikin jawabin nasa, shugaba Sata, ya kuma yi kira ga kasashen Asiya da su kara zuba jari a kasashen Afirka ciki har da kasar Zambia.

A wannan rana, Mr. Sata ya kuma halarci reshen taron dandalin tattaunawa na Boao na "neman bunkasar nahiyar gargajiya ta Afirka", inda ya yabawa babban sakamakon da Sin ta samu cikin 'yan shekarun da suka wuce ta fuskar tattalin arziki, da zamantakewar al'umma, tare da bayyana cewa, dole ne kasashen Afirka su yi koyi da kasar Sin daga fannoni da dama. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China