in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na son yin hadin gwiwa tare da Zambia a fannoni daban daban
2013-04-10 16:29:58 cri

Ran 10 ga wata, yayin da shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin Yu Zhengsheng ya gana da shugaban kasar Zambia Michael Chilufya Sata a birnin Beijing, ya bayyana cewa, kasar Sin na son ci gaba da yin hadin gwiwa tare da kasar Zambia, wajen karfafa musayar ra'ayoyinsu kan fasahohin inganta dimokaradiyya, da bunkasuwar tattalin arziki, da kuma tattaunawa kan raya hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu da dai sauransu, ta yadda za a iya inganta ayyukan bunkasa kasashen biyu da kuma zumuncin da ke tsakaninsu.

Shugaba Sata ya bayyana cewa, kasar Sin ta kasance wata abokiyar arzikin kasar Zambia tun tsahon lokaci, kuma a halin yanzu, kasar Sin na da kyakkyawan yanayin tattalin arziki, kasuwannin zuba jari, da kuma fasahohi na zamani. Don haka kasar Zambia na fatan kamfanonin kasar Sin, za su kara zuba jari a kasar, don bunkasa hadin gwiwar bangarorin biyu bisa fannoni daban daban.

Shugaba Michael Chilufya Sata ya kai ziyarar aiki a kasar Sin, ya kuma halarci taron dandalin tattaunawa na Bo'ao na Asiya na shekarar 2013 tun ranar 4 zuwa ta 11 ga watan Afrilu, bisa gayyatar shugaban kasar Sin Xi Jinping. Kuma wannan shi ne ziyarar aiki ta farko da shugaba Sata ya kai kasar ta Sin tun lokacin da ya hau ragamar mulki a shekarar 2011. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China