in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Libiya ta zargi Sudan ta baiwa 'yan adawa makamai
2014-09-07 20:43:17 cri
Gwamantin wucin gadi a Libya ta fidda wata sanarwa, dake cewa a 'yan kwanakin baya, wani jirgin saman sojin kasar Sudan ya keta sararin saman ta ba tare da neman izini ba, jirgin da Libiyan ta ce na dauke ne da wasu makamai da aka samar ga dakarun dake adawa da gwamnati. Mayakan da a halin yanzu ke ci gaba da mamaye birnin Tripoli fadar gwamnatin kasar.

Sanarwar ta kara da cewa kasar Sudan na kokarin tsoma hannu cikin harkokin gidan Libya, ta hanyar goyon bayan mayaka 'yan ta'adda a kasar, wanda hakan kai tsaye ya keta hurumin kasar ta Libya. Sanarwar ta kuma bayyana cewa, tuni gwamnatin wucin gadin kasar ta bukaci jami'an sojin Sudan da su koma kasarsu.

A daya hannun kuma, kasar Sudan ta gaskata cewa ita ce ta aike da wani jirgin sama na soja zuwa kasar ta Libya, amma ta ce jirgin na dauke ne da wasu kayayyakin da sojoji masu aikin sintiri na kasashen biyu dake yankin kan iyakar kasashen ke bukata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China