in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi allahwadai da karuwar tashin hankali a Libya
2014-08-18 09:41:37 cri

Tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD da ke Libya(UNSMIL) ta yi allahwadai da arangamar da ta wanzu ranar Lahadi tsakanin kungiyoyin 'yan tawayen da ke dauke da makamai a Tripoli, babban birnin kasar Libya, inda ta yi kira ga dukkan bangarori da su martaba kokarin da ta ke na ganin an tsagaita bude wuta.

Wata sanarwar da tawagar ta UNSMIL ta fitar, ta kuma bayyana takaicinta kan yadda fada tsakanin sassan biyu ya tilasta wa fararen hula da dama barin gidajensu yayin da wasu kuma suka jikkata baya ga kayayyakin da aka lalata

Bugu da kari tawagar ta bukaci sassan da ke arangama da juna da su amsa kiran da kasashen duniya ke yi dangane da kokarin da tawagar ta UNSMIL ke yi na ganin an hanzarta tsagaita bude wuta tare da kawo karshen zubar da jini da dakatar da asarar dukiyoyin da ake yi, ta yadda za a hanzarta magance matsalar da ake fuskanta a halin yanzu.

Tun a ranar 13 ga watan Yuli ne kasar ta Libya ta fara fuskantar kazamin tashin hankali tsakanin kungiyoyi masu kishin Islama da ke dauke da makamai da mayakan da ke goyon ra'ayin sakulanci a kokarin da suke na kwace birnin Tripoli.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China