in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane a kalla 10 sun rasa rayukansu a sakamakon rikicin da ya faru a birnin Benghazi na kasar Libya
2014-09-02 14:48:48 cri
Kakakin sojojin musamman na kasar Libya ya tabbatar a ranar 1 ga wata cewa, an yi arangama tsakanin sojojin da dakaru masu kishin addini a birnin Benghazi dake gabashin kasar Libya, lamarin da ya haddasa mutuwar sojoji a kalla 10.

Kakakin sojojin ya kuma bayyana cewa, dakarun Ansar al-Sharia masu kishin addini sun kai hari ga sojojin musamman na kasar a wannan rana ne a kokarin da suke na kwace ikon mallakar filin jiragen sama na Benina dake birnin Benghazi.

Ya ce, wannan dauki ba dadi ya haddasa mutuwar sojoji 10 a wannan rana, yayin da wasu guda 10 suka ji rauni. Sai dai sojojin musamman na kasar ta Libya sun samu galaba a kan dakarun sakamakon taimakon da suka samu daga sojojin saman kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China