in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyoyin Fajr Libya da Ansar Al-Sharia 'yan ta'adda ne inji majalissar kasar Libiya
2014-08-25 14:11:28 cri
Majalisar wakilan kasar Libya ta ayyana sunayen kungiyoyin mayakan sa kai na Fajr Libya, da Ansar al-Sharia a matsayin kungiyoyin 'yan ta'adda, tana mai cewa, za ta goyi bayan yakin da sojojin kasar za su yi da wadannan kungiyoyin biyu har sai sun dakatar da tada zaune tsaye.

Wata sanarwa da majalisar ta fitar a ranar 24 ga watan nan, ta bayyana yadda dakarun kungiyar Fajr Libya da na Ansar Al-Sharia suka kaddamar da hare-hare kan hukumomin gwamnatin kasar, tare da barnata ababen more rayuwar jama'a a biranen Tripoli da Benghazi.

Ci gaba da dauki ba dadi tsakanin sassan mayakan sa kai a kasar ta Libiya dai na da nasaba da gazawar da tsagin kungiyar 'yan kaifin kishin addini ya yi, na lashe zaben majalisar wakilan kasar a karshen watan Yunin da ya shude.

Kaza lika manazarta harkokin siyasar kasar na hasashen cewa, gwagwarmayar da masu tsattsauran ra'ayi da 'yan ba-ruwanmu ke yi, game da damke ikon muhimman yankunan kasar ne ke dada tsananta fadace-fadace da ke faruwa a halin yanzu, matakin da kuma ke kara dagula yanayin da kasar ke ciki. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China