in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yin gyare-gyare kan tsarin siyasar Hong Kong, harkokin cikin gida ne na kasar Sin, kada a tsoma baki cikinsu
2014-09-02 20:22:35 cri
Qin Gang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin a ganawarsa da manema labaru da aka yi yau Talata 2 ga wata ya ce, Hong Kong, wani yankin musamman ne na Jamhuriyar Jama'ar kasar Sin, kuma harkokin da ke shafar yin gyare-gyare kan tsarin siyasar Hong Kong, harkoki ne da yankin Hong Kong ke kulawa da su, kuma harkokin cikin gida ne na kasar Sin. Sin ba za ta yarda da a tsoma baki cikinsu ba.

Mista Qin ya bayyana cewa, kwamitin kula da harkokin waje na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ya aika da wata wasika zuwa ga takwaransa na majalisar wakilan kasar Birtaniya, saboda kwanan baya, kwamitin kula da harkokin waje na majalisar wakilan Birtaniya ya tambayi kasar Sin dangane da yadda take aiwatar da sanarwar hadin gwiwa ta kasashen Sin da Birtaniya.

Mista Qin ya tabbatar da cewa, kasashen Sin da Birtaniya sun tuntubi juna, inda Sin ta bayyana matsayinta a hukumance, lamarin da ya yi daidai kuma ya cancanta. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China