in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
NPC za ta tattauna kan batun da yankin Hong Kong ya gabatar game da 'yancin gudanar da zabe
2014-08-27 20:19:55 cri
Shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar Sin NPC Zhang Dejiang ya ce za a gabatarwa kwamitin majalisar wakilan jama'a wani daftari da yankin Hong Kong ya gabatar game da neman 'yancin al'ummar yankin na gudanar da zabe da kansu.

Ana saran zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'a ya tattauna wannan bukata kafin ya kammala zamansa a ranar Lahadi.

Zhang Dejiang ya ce, daftarin da yankin na Hong Kong ya gabatar yana son ya fara aiki ne a zaben jami'in farko na yankin na musamman da za a yi a shekarar 2017 da kuma zaben 'yan majalisa a shekara ta 2016.

Yanzu dai mambobin majalisar wakilan jama'a sun nazarci rahoton da jami'in farko na yankin Hong Kong na musamman ya gabatar game da gyaran fuska a harkokin zaben, ko da ya ke ba a yi wani karin haske game da sauran abubuwan da ke kunshe cikin daftarin ba.

A shekara ta 2012 ne kwamitin majalisar wakilan jama'a ya zabi jami'in farko na yankin na Hong Kong na yanzu, yayin da yanzu kuma yankin ke nemen a baiwa al'ummar yankin damar zaben shugabanninsu da kansu a zaben shekarar 2017. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China